Jarumar Mata

Jarumar Mata
By Hamisu Breaker

Ashe da rai nake son ki jaruma ba da zuciya ta ba
Komai ruwa da iska akan ki ba za na daina kewa ba
Idan na samu zarrar samun ki ba zani tanka kowa ba
Ni ban ga mai harara ba
Bare na waiwaya fa

In dai a kan ki ne za na jure wahalar zuwa garin nisa
Da an taba ki a jira ni don kau tilas na dau fansa
Jumirin jiranki nai don ki zo na kalle ki gimbiyar Hausa
Sirri na rayuwa ta kece kawai da kin kira da na amsa
Zuma a baki dadi gare ta kin bani taki na lasa
In dai a kan ki ne na yi nisa don ba kiran da zan amsa
Tilas ganin mu tilas barin mu qaunar ki tunda nai nisa
Sam ba batun na fasa ko za’a ce mani in bada rai fansa

Zarin zubin ki daidai ne
Ya kama zuciya ta ne
Ina jin kamar mafarki ne
Ina san ki so mataki ne

Ni banda damuwa in har zan bude yan idanu na
Kalle ki ga ki dab da ni toh me za ya damu qalbi na
Yau za na yo amo tunda na gane kina da tausai na
Don yanzu na zamo ya mafatauci mai bidar qurin kwana
Na kwallashe ladas sarar da iya maki ya kalamai na
Daga zuciya nake kwatanta ina zaiyano jawabai na
Idan babu ke ina ne zan saka zuciya ta bar yawan quna
Kowa da nasa amma ni kece cikar muradai na
Yau ga ni an ruwa kusa da kada zo ki ceci qarko na
Komai da maffita karda ki saba da furta bankwana
Ina ji ina gani yadda nake son ki ya fi qarfi na
Ina son a duniya da wanda ya ke janye duk tunani na
Soyayya rawuya wani sa’in sai ta zam wutar gona
Duk wanda ke cikin ta shine jurau amma fa a gurina
So na faranta rai da ruhi ya sa ka zam kamar sarki
Kuma rayuwa da so misali zai na kama da a mafarki
Samari muyi hakuri don har mun samu so mu sa sauqi
Yan mata muyi hakuri idan har mun samu so mu sa sauqi
Masoyi yana da rana ne
Masoyi yana da rana ne

Sarakuna

Sarakuna
By Naziru M Ahmad

Ba’a chinye toron giwa

Kai giwa da ranta toh sai dai kallo
Sarkin Kanonmu mai alfarma
Sarkin Zaria na nan shima
Sarkin Musulmi mai dumbin daraja
Sarakuna iyayen kowa ne

Ba’a chinye toron giwa

Kai giwa da ranta toh sai dai kallo
Sarkin Kanonmu mai alfarma
Sarkin Zaria na nan shima (gaishe ku)
Sarkin musulmi mai dumbin daraja (a’a)
Sarakuna iyayen kowa ne

Kare da kai bakwai sai kallo

Ita qarya fure take ba y’ay’a
Kamar mutum tana nan daidai
Ku yi shiga yana nan d’aid’ai
Kare da kai nakwai ko dad’a ne
Da ka gane shi ka san aljan ne

Zaki cikin awakai sarki

Kai kura da akuya sai dai kallo
Ruburbusa take ban taushi
Mai akuyar yana jin haushi
Ya labe da adda nan gefe
Yana jiranta ta kai ya kar ta

A gafara nace ga kyarkechi

Toh wannan batun yana chan baya
Girmansa ne kawai dan banza
Ga kwarjini kamar wata gabza
Ko akuya tana yi mai waigi
Da ta biyo shi sai dai yats tsere

Bara in waiwaya baya
In duba rayuwar baya
In binchiko hirar wata gawa

Sarki tura fa ta kai bango (iye)
Ka saka mu a loko
Zanche kake kamar wani soko
Hirar dabba muke yi ko waqa

Hirar Kanon kuke so ko Zazzau

A’a ka kyale baba ba kwa dan Zazzau
Na baya rauma komai sai doya

Idan ya ji ku kun san zai rama

Eh ko da ya jimu ba zai che shine ba
Ba shi a che mai dan Zazzau

Kuna nufin yana kalan dangi

Eh idan ya ji ko da ya haura (iye)
In yay yi Niger
Anka che Kano ne ko Zazzau
Sai yace Kanon nan ta fi su (gaske)
Ko manyansu don ba su so a gane sunansu (ku che da su)
Toh mu mun san su

Ya ake ana gane su

Toh mallam shigarsu mai ban tsoro che (ashe)
In sarki ne in ya taho kamar wani gwanki ne (gaske)
Sarkin Zazzau in ya shigo kamar wani giwa ne (gaishe ku)
A fagen mulki al’amuransa tamkar rana ne (haka ne uhm)
In ta haska duk duniyar ga kowa ya gane (iye)
Al’adunsu kamar ache mutanen farko ne (a’a)
Sarkin Zazzau ga tambura yau mun doka (hmm)
Naziru ne sarkin waqa (gaishe ku)
Ya shigo a Zaria gaisheka (uhn hm)
Lafia zaki ko wat taba ka yau sai ya koka

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

In gaida Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babban dutse qaryarsu fa su kawo ma raini

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babban jeji ko wab bache ciki sai dai ihu

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babban sarki wanda in ya tashi kowa zai miqe

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga sahun giwa taken su wa na mai tsoron aiki

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babbar fada baban sarakuna ‘ya’yan kirki

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Sarkin Musulmi Nazir sarkin waqa ne yake yi ma baiti

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Su dawisu masu ado
Sarkin garinmu mai kyan zamani
A Kanon dabo

Mu dai garinmu akwai ban mamaki

Lafia iska

Kowa ya kewaya zai sameka

Lafia tarko

Ko wash shigo ka zai sha mamaki

Ka ga dutsen murhu

Sai an aje ka ne za’ai dori
Sasarin alqali

Duk kan mazan gari na tsoron ka

Mai ado mai tsari

Dawisu yan gari na qaunar ka

Sarkin dabo
Mai martaba da alfarma
Mai wa diyansa ne hidima
Mu dai sarakuna yau mun samu
Sarakuna iyayen kowa

Mu daki tamburan sarki nazbi

Sarkin waqar da duk duniya duk an san shi
Mai kayan yaqin da duk duniya ke tsoron shi
Mai girma nazbi jama’arka na nan damanka
Shiga da kanka mai komai naira
Sarkin waqa a duk duniya na gaishe ka
Mu daki tamburan sarki nazbi

An baku mota yara
Sarkin waqar da duk duniya duk an san shi (uh hm)
Mai kayan yaqin da duk duniya ke tsoron shi (gaishe ku)
Mai girma nazbi jama’arka na nan damanka
Shiga da kanka mai komai naira (ga miliyan biyu ku sha mai)
Sarkin waqa a duk duniya na gaishe ka
Ga sarkin waqa (wane)
Baban Islama (gaske)
Mai haqora na azurfa maqogaronsa tamkar zinari (gaskia ne)
Fannin waqa (hmm)
Kun ga shi ya gawurta
In kana jin muryarsa sai kace kana susar kunne (sarki yana ji)
Don dadinta (ashe)
Shi ya gawurta (sarki)
Al’amuransa sai ikon Allah (ashe kaima sarki taka zata)
Lafia na hazbi
Sannu baban Islama (an hada maku da dawakai)
Buhun qaya sam ba’a chiko
In an chika ka kuma ba’a danne (gaskia ne)
In an danna mutum ya soke hannunsa (gaskia ne)
Ba wanda ya tsaya ma sai Allah balle mutum yace sai ya kar ka (sarki ya gode)
Babu mai ma sai Allah balle mutum yache yau ya daina (gaskia ne)
Allah ka kyautata karshenmu
Ameeeeen