Aure Da Kudi

Aure Da Kudi
By Babangida Kakadawa

Yau na yi tagumi na rame ban iya cin komai
Allah koro, Allah koro da masoyiyata
Rashin ganinta na rame bana iya cin komai
Yau ga dan talakawa yana son yar mai kuddi
In na biya sadaki ni ba za ni yi lehe ba
Da na biya sadaki ni ba za ni yi lehe ba
Idan taje gidana ba zan bar ta a tsumma ba
Dada amman wata qil lallai babanta za zai so ba mamarta ba ta so ba
Matan garinga sun yi yawa kuma sun cika tunbulbul
Kuma ba su son aure sai sun bidi kuddi
Idan baka da kuddi bana ba zaka yi mata ba
Idan kana da kuddi, in sun ganka da mota har hotuna suke kaima
Darje bidi mai kwari
Tsoho da kudi yaro
Yaro in ba kuddi yau ya koma tsoho

Ana wata magana jama’a ga wata magana ta zo
Wani mai jaki ya ingiji mai goyo, babbar magana annan
Ji ana wata magana jama’a ga wata magana ta zo
Wani mai jaki ya ingiji mai goyo, babbar magana annan
Ji samari na son mata kuma sannan ba kuddi
Gayu na son mata bana gayu ba kuddi
Sai zama a kan hanya da takama da sa T-shirt
Sai zama a kan hanya da takama da sa 2-pac
In sunka ga mata wadansu na fadin chika, wasu na fadin chizga
Muna nan muna aikin ba zamu tsayawa ba
In ka ga tsayawata sai in mutuwa ta zo
Babangida Kakadawa mai kida kanen Sani
Na Dan Maraya wakar wa kayi sai mu
Dukan zare yana tsinkewa banda irin nau wa
Don nau zaren da yar murde ya zama karfen jirgi
Qirarsa sai maqeran asaili su yi ke horo nai, ga mu
Don da dan haye da dan gado ba zasu zame dai ba
Yaro bai son yaro ne ba
Yaro bai son yaro ne ba sai ya rasa baba nai ko ya rasa mama tai zai san yaro ne shi
Ku ji dai yana ganin duniyar nan tai masa talala har da fadin wai sune zasu yi ba mu ba
In banda rashin kunya, mai bidar nama mi kai shi zuwa gulbi wai har da yuqaqe nai
Mai bidar kifi mi ya kai shi zuwa kwata, mi ya kai shi zuwa zango kuma harda zugun taru
Tsohuwar kura mai bidar kashin bango, wancan na kan gina, in ta ga mai tsoka ba zata raga mai ba
Thohuwar kura sai dai ki ci kan ki, ni ba za ki ci na ba, yalum
Alhaji Babangida Kakadawa mai kida kanen Sani
Na Dan Maraya wakar wa kayi sai mu

Yau na yi tagumi na rame ban iya cin komai
Ga dan talakawa yana son yar mai kuddi
Da na biya sadaki ni ba za ni yi lehe ba
Idan taje gidana ba zan bar ta a tsumma ba

Ina So In Yi Aure

Ina So In Yi Aure
By Babangida Kakadawa

Mai madi ka tallar zaqi
A’a toh shi kam mai zuma gida ya ke zaune ne
Ku fa malamai ku dauko littafanku tunda dai kune ne manya
Ku karanta ku fassara mana aya
A yanzu dai shine dai dai

Musulunci akwai nasiha a cikinsa
Wanda kuma Allah ya so
Manzon Allah yayi
Amma yanzu mun tsiro da al’adunmu
Masu son lalata mu
Don yau ba a baka aure ba kuddi
Wai su sun fi so su bai wa mai taqama da adda a cikin gida
Yana datse hannu
Suna samun kudi
Sannan za su bashi mata kyakykyawa

Ga ni ni kuma Babangida
Ina so in yi aure
Ina son auren diyan kabawa Babangida
Ni kuma ga ni bani yin minti dai ruwa

Ina son in yi aure
Ina son auren badakkara ni Babangida
Ni kuma ga ni ban da walki gindina

Ina son in yi aure
Ina son auren basakwkwata ni Babangida
Sannan nig a nib a batoranki ne ba

Ina son in yi aure
Ina son auren Fulani Babangida
Ni kuma ga ni ban da shanu ba rugga

Ina son in yi aure
Ina son auren Bagobira yar Gobir
Amma ni ba ni son ace bawa ne ni

Ina son in yi aure
Ina son auren Bazazzaga ni Babangida
Ni kuma ba ni cin faten doya kullum

Ina son in yi aure
Ina son auren Babarbara ni Babangida
Sissan nan na gwal ke sa ni ina sauna

Ina son in yi aure
Ina son auren Bakambara ni Babangida
Ni kuma ga ni bani son daukar kaya

Ina son in yi aure
Ina son auren diyan Kanawa Babangida
Ni kuma ga ni ban da tsagen baki
Sannan ni ga ni ba gajere ne ni ba

Ina son in yi aure
Ina son auren Bakatsina ni Babangida
Katsinawa na dikko dakin kara
Kunya garesu ba dai tsoro ba
Ina son auren Bakatsina ni Babangida
Ni kuma ga ni bani son yaqi ko kusa

Ina son in yi aure
Ina son auren Bazamfara ni Babangida
Ita tana qaunata ni ina ra’ayinta
Ubanta sai yacce a’a

Ita tana qaunata ni ina ra’ayinta
Ubanta sai yacce um um

Wani da bata qauna wai das hi za’ayi aure
Toh don Allah a daina auren dole
Saboda auren tilas kasa diya yawon banza

Ba wulaqantarce a yanzu sai marar ilmi
Ko wai ilmi ku gane ya kece raini
Ba wani mai yi mai

Da sana’a
Da fahimta
Kowa da wadda Allah nayyo mai

In sahiya ta waye
Wadansu na aikin gona
Wadansu suna office
Wadansu karatu
Wadansu ko waqa sun kai
Hakanan Allah yas so

Tsuntsu asalin gidansu kan icce ne
Kifi asalin gidansu bai wuce rafi ba

A’a ni dai Babangida
Duniya ko tai man kida b azan taka ba
Duk wanda ya taka ya ga kwan

Cin hakin sama sai raqumi
Awaki ku ci kyasuwa
Ku ko ku yi hankuri
Inda Allah bai kai mutum ba qaqa zai kai can

Akuya ba ta layya in ga rago
Duk na Annabi na san ba zai lalace ba