Dan Kwali

Dan Kwali
By Sogha Niger

Dan kwaliiii
Ga wakar dan kwali

Dan kwaliiii
Ga wakar dan kwali

Iye nanaye ayye iye iye nanaye
Ayye iye iye nanaye dan kwali

Wai ni mareni, wai ni mareni, wai ni mareni
Wai ni mareni na ban tausai
Ba ta da inna ba ta da abba
Ba ta da sarmayin da ka sai mata dan kwali

Iye nanaye ayye iye iye nanaye
Ayye iye iye nanaye dan kwali

Dan kwali iri da iri ne

Babu wanda ban darma ba
Sai wancan na hanyar kwanni mai rabasha

Iye nanaye ayye iye iye nanaye
Ayye iye iye nanaye dan kwali

Ina tahiya ta
Sai tarar da malam zamne
Sai ya tokare ni da allo
Sai na hwadi bayan darni
Sai na haihi dana Bube
Amman bani ce mashi Bube
Sai dan malami da karatu da turanci

Iye nanaye ayye iye iye nanaye
Ayye iye iye nanaye dan kwali

A can da dauri
Anka ce yau wasa
Yan mata su sanyo kwalli
Sauran sai su sa jan-baki
Sai a hadu hilin wasa
Samari sai suna wilgawa
Ka ga wadda ranka yake so
Hittila ce kake matsawa
Rawa da waka rannan sai sahe

Iye nanaye ayye iye iye nanaye
Ayye iye iye nanaye dan kwali

Dan kwaliiii
Ga wakar dan kwali

Dan kwaliiii
Ga wakar dan kwali

A can da dauri
Anka ce yau wasa
Yan mata su sanyo kwalli
Sauran sai su sa jan-baki
Sai a hadu hilin wasa
Samari sai suna wilgawa
Ka ga wadda ranka yake so
Hittila ce kake matsawa
Rawa da waka rannan sai sahe

Iye nanaye ayye iye iye nanaye
Ayye iye iye nanaye dan kwali

Dan kwaliiii
Ga wakar dan kwali

Dan kwaliiii
Ga wakar dan kwali

Samarin Shaho

Samarin Shaho
By Sogha Niger

Soooyayyaaaaaa…
Allah ya bar soyayya
Soyayyaaaaa…

Soyayya kala kala ce
Soyayya iri iri ce
Soyayyan maso wani cuta
Kai kowa ya son mai so nai

Samarin shaho hankali da samarin shaho yan’mata

Yan’mata ku duba sosai
Ku sa hankali ku gane samari
Ku gane samarin kirki
A nan cikin masoyan naku
Ma su son ku da niyyar kirki
Don yan yaudara suna da dama
Sune samarin shaho

Samarin shaho hankali da samarin shaho yan’mata

Yan yaudara samarin shaho
Ganin kitse a ke wa rogo
In kin ganine su tsab sun shirya (lab lab lab)
Ga su wajen ki
Wannan magana mai dadi
Iya jan hankali yan’mata (toh)
Hattara yarinya
In bakki da dogon dubi
Da nazari da yin lissahi
Zai shirya gadar zare ram
Da kin hau ta kin hwada rami

Samarin shaho hankali da samarin shaho yan’mata

Soyayyan maso wani cuta
Kowa ya son mai so nai
Mai son ka baya sa lubutar ka
In dadi in wuya ga ku tare
Nema yake duk sahe
Allah ya kai ku hwagen aure (samarin kirki)
Allah ya kai ku hwagen aure (samarin kirki)
Eh Allah ya kai ku hwagen aure (samarin kirki)

Eh samarin shaho
Ku dibi idanun nashi
Ku dibi kahwahun nashi
In ka gane shi tsab ya shirya
Lab lab lab ga shi wajen ki
Wannan magana mai dadi
Iya jan hankalin yan’mata
Toh hattara yarinya

Ko kaine samarin shaho
Ku dibi idanun nashi
Ku dibi kahwahun nashi
Ko kaine samarin shaho
Ko kaine samarin shaho
Ehhhh (can dai)

Yan yaudara samarin shaho
Ya buge ki ki hwadi ya tsere
Ya bar ki nan kina wayyoh Allah
Ya cuce ni ya cuce ni

Ya cuce ni ya tahi ya bar ni
Ya cuce ya tahi ya tahi

Soyayyan maso wani cuta
Kowa ya son mai so nai
Mai son ka baya sa lubutar ka
In dadi in wuya ga ku tare
Nema yake duk sahe
Allah ya kai ku hwagen aure (samarin kirki)
Allah ya kai ku hwagen aure (samarin kirki)
Eh Allah ya kai ku hwagen aure (samarin kirki)

Uban Gida na

Uban Gida na
By Aminu Ala

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

In ban da bautar zuciya da bata tsirarwa
Ya za na tara abincin da ba ni cinyewa
Ya za na gina gida wanda ba shi dorewa
Ya za na tara tufafin da ba ni sanyawa
Ya za na dassa hasashen da ba shi dorewa
Ya za na shinfida daula da ba ta dorewa
Ya za na daura majanyin da ba za ya suncewa
Uban gida na da zaka dauki zance na
Da ka yi gyara kafin a gincire kwana

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Yey in banda bautar zuciya da ke halakkarwa
Abin hawa na ya zarce na hawan kowa
Rigar sakawa ta zarce ta jikin kowa
Gami da takalma sun fi kafar kowa
Dangi agogo na ya fice ta gun kowa
Daidai da zobe na ya fi hasashen kowa
Hatta da biro na alqalam na zannawa
Uban gida na da zaka dauki zance na
Wallahi da an gyara da tsakkiyar rana

Uhmm gida dubu na gina tanadin wajen kwana
Ciki da falo dubbai daban daban dana
Don tanadi na talauci da ke tsumin rana
Sannan in kauce wa idanduna da ke bina
In badda sawaye na ga masu bi kona
An dauke duniya mai tabbata gidan kwana
Gida ga mai burin rayuwa gidan gona
Uban gida na da zaka dauki zance na
Wallahi Allah da ka cikan muradi na

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Yey mun zam bayi na ciki da ba shi turewa
Muna haqaya na mai rijiya da babu ruwa
Muna nutsewa qasa zuciya ta na qawa
Muna ta bautar gangar cikin mu ba qiwa
Muna biyewa al’aura muna tsiyacewa
Giya ta rai ta sa muna qara rudewa
Ina tunani da sani da ke a kwakwalwa
Uwar gida na da kin fahimci zance na
Wallahi Allah da an rufe tunani na

Ni zuciya ta kuma ta hana ni yin barci
Dare da rana kuma ba ragi na sassauci
Tana ta kakabi ko abinci ba ta ci
Cikin ta mamaki ya game ta ga qunci
Sannan tunani yai tarnaqi gadon barci
Ina ta mamaki kan hali na zalunci
Baqin maciji da ake kira da kumurci
Uban gida na bisa qarqashin tunani na
Yafe mu jin qan tsare nasa a tunani na

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Duk inda ka ga qasa kan ture a kan ilmi na
Toh arziki da Buwayi ya basu dangi na
Ya zarce dukka buqatu na su da an tona
Sai dai idan jagoran su ya zamo bauna
Sai babu adalci gun su shugabanni na
Idan da adalci babu mai shiga rana
Kowan su ya zarce wa jibin sa dangi na
Ya shugaba na in an nazar a zance na
Wallahi Allah ya tseratar da mu quna

Hannun ka mai sanda yau na ke iyaye na
Nuni da nishadi nake wa baba na
Yau gyara kayanka ba shi maida mu rana
Ya shugaba na in har ka dauki zance na
Abin da ka tara ka aje gidan kwana
Da wanda ka yi bushasha kake tsumin qauna
Toh wanda ka bayar za shi yayi ma rana
Uban gida na in yanzu ka ga laifi na
Ai za ka gane ran tsaida mu cikin rana

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Ku taimaka mini gun dakatar da kuka na
Don kar na qarar da ruwan cikin idanu na
Suna da rana a gaba zubar hawaye na
Wai shin kwa ruhi da jiki da hankali da na
Sun yarda ranar tsayuwa tana tsumin kwana
Wai shin kwa labari na wuta da aljannah
Anya bani Adam ya aminta ko ni da na
Ya shugaba na da ka amince zance na
Mai za ya rude ka da handama tsakar rana

Uban giji na afuwar ka ni nake nemaaaaaaaaaa
Uban giji na gafarar ka ni nake nema
Uban giji na afuwar ka mu muke nema
Uban giji na sauqin ka ne abin nema
Uban giji na rahamar ka mu muke nema
Uban giji na gafarar ka mu muke nema
Uban giji na ceton ka mu muke nema

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Uban gida na da zaka dauki zance na
Aradu Allah da ka haye hasashe na

Ciwon Idanu na

Ciwon Idanu na
By Umar M Shareef

Ciwon idanu na
Ki yi mani magani
Ine maki godiya
Kin ji masoyiya ta

Ciwon idanu na
Kayi mani magani
Ine maka godiya
Ka ji masoyi na

Amshe kiran da nai miki kiyi mani lamuni
Na makance idanu na ba sa gani
Na bi yi zafi na bi sanyi ke nake son gani
Kin ji sautin ki kawai shi zai warkar da ni
A rashin lafia na niyo kwanciya
Maganar gaskia ke ce magani na

Ciwon idanu na
Kayi mani magani
Ine maka godiya
Ka ji masoyi na

Ga ni da batutuwa don ke na tanada
Ba ni da gurin zuwa in ba kya gida
Ke zan kawo wa komai kika yo bida
Ba na mantuwa zance in kin fada
Kine mani kwarjini in da nake gani
A so son bayani ko ga abokai na

Ban jin zagar qawaye a soyayya kai na dauka
Ka share mani hawaye ka sa na daina kuka
In dai ina a raye sam ba na barin ka
Allahu ya kiyyaye ba ni son wanin ka
Kai ne dai daya a cikin zuciya
Mai saka ni dariya sannu masoyi na

Ciwon idanu na
Ki yi mani magani
Ine maki godiya
Kin ji masoyiya ta

Za ni zamo uwa cikin zuriyar ka
Za ni zamo surrika gun mahaifiyar ka
Ba ni barin damuwa ta isso gare ka
Babu jira dariya nai shirin ba ka
Ba ni so kai fushi na dau alwashi
Barin ka da qishi in ka shigo gida na

Ba ni so a mini zance in ba na ki ba

Ba ni so a mini kyauta in ba naka ba

Za ni rassa rai idan aure ba’a bani ba

Ban shirin zama da kowa in ba kai ne ba

Maganar gaskia a cikin zuciya
Ke ce ke daya ni na addana

Haaaaa Haaaaa

Jarumar Mata

Jarumar Mata
By Hamisu Breaker

Ashe da rai nake son ki jaruma ba da zuciya ta ba
Komai ruwa da iska akan ki ba za na daina kewa ba
Idan na samu zarrar samun ki ba zani tanka kowa ba
Ni ban ga mai harara ba
Bare na waiwaya fa

In dai a kan ki ne za na jure wahalar zuwa garin nisa
Da an taba ki a jira ni don kau tilas na dau fansa
Jumirin jiranki nai don ki zo na kalle ki gimbiyar Hausa
Sirri na rayuwa ta kece kawai da kin kira da na amsa
Zuma a baki dadi gare ta kin bani taki na lasa
In dai a kan ki ne na yi nisa don ba kiran da zan amsa
Tilas ganin mu tilas barin mu qaunar ki tunda nai nisa
Sam ba batun na fasa ko za’a ce mani in bada rai fansa

Zarin zubin ki daidai ne
Ya kama zuciya ta ne
Ina jin kamar mafarki ne
Ina san ki so mataki ne

Ni banda damuwa in har zan bude yan idanu na
Kalle ki ga ki dab da ni toh me za ya damu qalbi na
Yau za na yo amo tunda na gane kina da tausai na
Don yanzu na zamo ya mafatauci mai bidar qurin kwana
Na kwallashe ladas sarar da iya maki ya kalamai na
Daga zuciya nake kwatanta ina zaiyano jawabai na
Idan babu ke ina ne zan saka zuciya ta bar yawan quna
Kowa da nasa amma ni kece cikar muradai na
Yau ga ni an ruwa kusa da kada zo ki ceci qarko na
Komai da maffita karda ki saba da furta bankwana
Ina ji ina gani yadda nake son ki ya fi qarfi na
Ina son a duniya da wanda ya ke janye duk tunani na
Soyayya rawuya wani sa’in sai ta zam wutar gona
Duk wanda ke cikin ta shine jurau amma fa a gurina
So na faranta rai da ruhi ya sa ka zam kamar sarki
Kuma rayuwa da so misali zai na kama da a mafarki
Samari muyi hakuri don har mun samu so mu sa sauqi
Yan mata muyi hakuri idan har mun samu so mu sa sauqi
Masoyi yana da rana ne
Masoyi yana da rana ne

Sarakuna

Sarakuna
By Naziru M Ahmad

Ba’a chinye toron giwa

Kai giwa da ranta toh sai dai kallo
Sarkin Kanonmu mai alfarma
Sarkin Zaria na nan shima
Sarkin Musulmi mai dumbin daraja
Sarakuna iyayen kowa ne

Ba’a chinye toron giwa

Kai giwa da ranta toh sai dai kallo
Sarkin Kanonmu mai alfarma
Sarkin Zaria na nan shima (gaishe ku)
Sarkin musulmi mai dumbin daraja (a’a)
Sarakuna iyayen kowa ne

Kare da kai bakwai sai kallo

Ita qarya fure take ba y’ay’a
Kamar mutum tana nan daidai
Ku yi shiga yana nan d’aid’ai
Kare da kai nakwai ko dad’a ne
Da ka gane shi ka san aljan ne

Zaki cikin awakai sarki

Kai kura da akuya sai dai kallo
Ruburbusa take ban taushi
Mai akuyar yana jin haushi
Ya labe da adda nan gefe
Yana jiranta ta kai ya kar ta

A gafara nace ga kyarkechi

Toh wannan batun yana chan baya
Girmansa ne kawai dan banza
Ga kwarjini kamar wata gabza
Ko akuya tana yi mai waigi
Da ta biyo shi sai dai yats tsere

Bara in waiwaya baya
In duba rayuwar baya
In binchiko hirar wata gawa

Sarki tura fa ta kai bango (iye)
Ka saka mu a loko
Zanche kake kamar wani soko
Hirar dabba muke yi ko waqa

Hirar Kanon kuke so ko Zazzau

A’a ka kyale baba ba kwa dan Zazzau
Na baya rauma komai sai doya

Idan ya ji ku kun san zai rama

Eh ko da ya jimu ba zai che shine ba
Ba shi a che mai dan Zazzau

Kuna nufin yana kalan dangi

Eh idan ya ji ko da ya haura (iye)
In yay yi Niger
Anka che Kano ne ko Zazzau
Sai yace Kanon nan ta fi su (gaske)
Ko manyansu don ba su so a gane sunansu (ku che da su)
Toh mu mun san su

Ya ake ana gane su

Toh mallam shigarsu mai ban tsoro che (ashe)
In sarki ne in ya taho kamar wani gwanki ne (gaske)
Sarkin Zazzau in ya shigo kamar wani giwa ne (gaishe ku)
A fagen mulki al’amuransa tamkar rana ne (haka ne uhm)
In ta haska duk duniyar ga kowa ya gane (iye)
Al’adunsu kamar ache mutanen farko ne (a’a)
Sarkin Zazzau ga tambura yau mun doka (hmm)
Naziru ne sarkin waqa (gaishe ku)
Ya shigo a Zaria gaisheka (uhn hm)
Lafia zaki ko wat taba ka yau sai ya koka

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

In gaida Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babban dutse qaryarsu fa su kawo ma raini

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babban jeji ko wab bache ciki sai dai ihu

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babban sarki wanda in ya tashi kowa zai miqe

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga sahun giwa taken su wa na mai tsoron aiki

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Eh gaisuwa ga babbar fada baban sarakuna ‘ya’yan kirki

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Sarkin Musulmi Nazir sarkin waqa ne yake yi ma baiti

Sarkin Musulmi na Sokoto mai ado mai makaman yan yaqi

Su dawisu masu ado
Sarkin garinmu mai kyan zamani
A Kanon dabo

Mu dai garinmu akwai ban mamaki

Lafia iska

Kowa ya kewaya zai sameka

Lafia tarko

Ko wash shigo ka zai sha mamaki

Ka ga dutsen murhu

Sai an aje ka ne za’ai dori
Sasarin alqali

Duk kan mazan gari na tsoron ka

Mai ado mai tsari

Dawisu yan gari na qaunar ka

Sarkin dabo
Mai martaba da alfarma
Mai wa diyansa ne hidima
Mu dai sarakuna yau mun samu
Sarakuna iyayen kowa

Mu daki tamburan sarki nazbi

Sarkin waqar da duk duniya duk an san shi
Mai kayan yaqin da duk duniya ke tsoron shi
Mai girma nazbi jama’arka na nan damanka
Shiga da kanka mai komai naira
Sarkin waqa a duk duniya na gaishe ka
Mu daki tamburan sarki nazbi

An baku mota yara
Sarkin waqar da duk duniya duk an san shi (uh hm)
Mai kayan yaqin da duk duniya ke tsoron shi (gaishe ku)
Mai girma nazbi jama’arka na nan damanka
Shiga da kanka mai komai naira (ga miliyan biyu ku sha mai)
Sarkin waqa a duk duniya na gaishe ka
Ga sarkin waqa (wane)
Baban Islama (gaske)
Mai haqora na azurfa maqogaronsa tamkar zinari (gaskia ne)
Fannin waqa (hmm)
Kun ga shi ya gawurta
In kana jin muryarsa sai kace kana susar kunne (sarki yana ji)
Don dadinta (ashe)
Shi ya gawurta (sarki)
Al’amuransa sai ikon Allah (ashe kaima sarki taka zata)
Lafia na hazbi
Sannu baban Islama (an hada maku da dawakai)
Buhun qaya sam ba’a chiko
In an chika ka kuma ba’a danne (gaskia ne)
In an danna mutum ya soke hannunsa (gaskia ne)
Ba wanda ya tsaya ma sai Allah balle mutum yace sai ya kar ka (sarki ya gode)
Babu mai ma sai Allah balle mutum yache yau ya daina (gaskia ne)
Allah ka kyautata karshenmu
Ameeeeen

Soyayya Dadi

Soyayya Dadi
By Adam A Zango

Eyy soyayya dadi idan har da ke zana yi
In ba ke wa zani kalla a bayan rai

Soyayya dadi idan har da kai zana yi
In ba kai wa zani kalla a bayan rai

Bayan rai sai mutuwa ajali dole
Riga ce babu guda wanda zai tube

Mai so na daure ki juyo na kalle ki
Don murna zan cika raina da mamaki
Kin yarje na kama gefen mayafinki
Dacena kin ban wuri ranki na zauna

Bayan rai sai mutuwa ajali dole
Riga ce babu guda wanda zai tube

Doka tambarin qauna taurarona mai haska samaniya
Zo ka cika burina ka yarda da ni hannunka na dan riqe

Iye zo ki cika burina ki yarda da ni hannunki na dan riqe

Ba ku ji bayani ba taurari ne ado na samaniya
Bisa sama in sun ka so haske nasu sai ya kewaye duniya

Iye cikin ido sahiba kin yi kwarjini
Tun haduwarmu na yo farin gani
Babu nadama ko da na sani
Daga haka mun ka hadu qauna ta dadu sai so ba fariya

Bisa sama in sun ka so haske nasu sai ya kewaye duniya

Na ji dadi ne gari da can haka an sa min mari
Murmushin alkawari zan yi miki babu saraurari

Na ji dadi ne gari da wuyar so gara shiga haure
Murmushin alkawari zai sam abun alfahari

Zan tsaya tare da kai zan baka kula ba sake (Bayan rai)
Kayanka na cancana in babu sai in sha rake (Bayan rai)
Alfarmata da kai inuwar ka ka barni ina fake (Bayan rai)
Bayan rai babu ni laifi in na yi ka haquri

Na ji dadi ne gari da wuyar so gara shiga mari
Murmushin alkawari zai zamabin alfahari

Eyy soyayya dadi idan har da ke zana yi
In ba ke wa zani kalla a bayan rai

Soyayya dadi idan har da kai zana yi
In ba kai wa zani kalla a bayan rai

Bayan rai sai mutuwa ajali dole
Riga ce babu guda wanda zai tube

Mata Ku Dau Turame

Mata Ku Dau Turame
Nazir M Ahmad

[Chorus]

Mata ku dau turame ya yi
Kuma ku ce nadi dai anyi
Sarki Kano Sanusi na II
Duniya tai dadi
Kuma ku ce Kano Dan Lamido
Uban matasa yayi

Wannan kidi kidin mata ne
In namiji ya taka yawa ne
Dada mu bar su suyi sha’aninsu
Mu dai muce Kano Dan Lamido
Uban matasa yayi

Mu dai mu ce Kano…
Kano…
Kano Dan Lamido

Chorus

A’a nace ku ce Kano…
Kano..
Kano Dan Lamido

Chorus

Kai farin ciki mutane rairai

Eyy mu bayyana mu jero daidai
Mu tara tara taro dai-dai
Mai takura da takon Lamido
Sanusi babban sarki

Kai ana daka ana Dan Lamido

Eyy ashe zuma tana nan zai-zai
Suma mabi bin ta zai-zai zai-zai
Ga shi muna kidan Dan Lamido

Kai mu kada kai muna Dan Lamido

Eyy Kano Dan Lamido
Na ce ku kada kai ana Dan La
Sarkin Kano Dan Lamido
Ga shi ana ta za.. Kano.. Kano
Ga shi Muna ta murna da sanusi
Sanusi mai Kano Dan Lamido

Chorus

Toh mazan kwarai suna bisa aiki
Matan kwarai kau kullun aiki
Wannan kida kidan mata ne
Yawan kidan na mai gata ne
Talaka mai kudi dai-dai ne
Ku doka tamburan Allah raini
Sarkin Kano matarar yaqi
Kun ga tsakin tama Dan Audu
Mai ilimi kuce insanu
Da ya fito a kwana da nunin
Qasan saninsa kullum yafun
Ba aljani bare ifritu
Maza jiran maza Dan Audu
Ko ma su qin ka sai sun so ka
Tunda Rabbi ya baka
A ko a kwance kai barcinka
Ja mu je zuwa sarkinmu
Babanmu mai tsare kukanmu
Taho mu je zuwa dan baiwa

Chorus

Ku dai mu ce Kano…
Kano..
Kano Dan Lamido

Chorus

Da na ji gangunan sun tashi
Sai in kira Yarima in gama
Da na ji dunyar ta dauke
Sai in kira Yarima in gama
Ruwan dollar yane man dai-dai
Wannan sakin ya ne Dan Lamido

Chorus

Toh ku zo mu je ga Sardaunan Dutse
Ehh Sardaunan Dutse
Nace da Sardaunan Dutse
Jallah mai kwana sallah
Jarman Wudil yana nan shima
Kuma ya na ta jin Dan Lamido
Sanusi babban sarki

Chorus

Dada e kai mu tafa hannuwa sai Lamido
Ehh Kano Dan Lamido
Kai mu bashi hannuwa Dan Lamido
Sarkin Kano Dan Lamido
Kai mu kada kai muna Dan Lamido
Ehh Kano Dan Lamido
Nace kai ku kada kai ana Dan Lamido
Sarkin Kano Dan Lamido
Kun ga muce Kano Dan Lamido
Uban matasa ya yi
Allah shi taya ka riqo (amin)

Wazobiya

Wazobiya
By Adam A Zango

Wazobiya…
Rayuwa sai da naira
In babu naira
Toh ko ka zam kwalele

Eyyyy yeh yeh yeeeh
Ey a hayye sama ado kasa kudi yan’matan duniya
A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)

Ehh Allah bani kudi in sai gida in je aikin Hajji (wazobiya)
Jama’armu ku saurara cikin kidanmu ba ma yaudara (wazobiya)
Kidan na bahaushe ne waqar ta Hausa ce kuma ba dabo (wazobiya)
Kalangu dan Hausa da ba’a yi mai jan kunnuwa (wazobiya)
Idan baku gane ba ina nufin Bature nai nufi (wazobiya)
Don ko da ya ji zai jinjina wa Hausa da al’uma

Ehhhhhhh
Yar yar yar lale lale kalangu shine kida

Ey a hayye sama ado kasa kudi yan’matan duniya
A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)

Ehh Allah bani kudi in sai gida in je aikin Hajji (wazobiya)
Mata nayi kira gaba dayanku sai ku yi tarbiya (wazobiya)
Duk kyawon mace in bada kyan halin kyawon kawai (wazobiya)
Mata kuyi aure ku dena zagayawan bariki (wazobiya)
Toh ga wata tai kwantai saboda kun ga bata da tarbiyya (wazobiya)
Yawan tarnaqiya yana ba mazaje sha’awa
Lai lai lale lale kalangu shine kida

A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)
Ehh Allah bani kudi in sai gida in je aikin Hajji (wazobiya)
Samari nayi kira a duniya ku bar yin yaudara (wazobiya)
Idan kunje tadi ku daina latsa yan’mata haka (wazobiya)
In ko kun qi ji toh in kuka haihu sai an maku (wazobiya)
Toh samari muyi sana’a mu daina dauke-dauke ga al’ummah
Toh duk nairar gaye idan da dan-hali nairar kawai (wazobiya)
Toh samari kuyi aure nai kira ku daina ruwan ido
Lai lai lale lale kalangu shine kida (eh.. ah.. ah.. toh..)

Ehh Allah bani kudi in sai gida in je aikin Hajji (wazobiya)
Kai ka ji kidan naira da ko mahaukaci na rausaya (wazobiya)
Duk tsufan tsoho idan ya ganta sai yai rausaya (wazobiya)
Toh kogi ya kawo ku zo mu sanya gora muyi hito (wazobiya)
In dai naira ce da ka biye ta yanzu ka bata (wazobiya)
Naira mai sa fada da uwa da uba kai duniya (wazobiya)
In dai kana da naira gidanku kai ne alhaji (wazobiya)
Ko da kai laifi gidanku babu mai yi ma fada
Lai lai lale lale kalangu shine kida

Lai lai lale lale kalangu shine kida
Ehh Allah bani kudi in sai gida in je aikin Hajji (wazobiya)
Yaran zamani kuje ku yo karatu ya fi kyau (wazobiya)
Kai duk gayun gaye in babu ilimi hoto kawai (wazobiya)
Iliminmu na addini da boko ya zama garkuwa (wazobiya)
Toh mata kuyi ilimi domin ku bai wa ya’ya tarbiya (wazobiya)
Yarinya kyakykyawa ku zo ku ganta amma ba aji (wazobiya)
Ba Arabi ba boko cikin gidansu ta zama akuya meh (wazobiya)
Idan za’ai aure a dunga bincike kar ai tumun dare
Lai lai lale lale kalangu shine kida (ahah!)

Akwai wasu na magana da ni da Zango ba yan Hausa ba (wazobiya)
Kuce wacece ce kuce mai kar ce ta rage wa baqin ciki (wazobiya)
Idan kuma caca ta ci ta samu kurciya don suyi ciro (wazobiya)
Idan baka gane ba ka zo da Hausa zan ma tambaya (wazobiya)
Idan ka ban amsa in tarbatar bahaushe ne kake (wazobiya)
In dai a Hausa ne gidanmu babu baubawan bara (wazobiya)
Toh barewa ta yi burus cikin birgimarta a bariya (wazobiya)
Bar barna bara na Kare wa ke bin mutum ba tarbiyya (wazobiya)
Lai lai lale lale kalangu shine kida

Eyyyy yeh yeh yeeeh
Ey a hayye sama ado kasa kudi yan’matan duniya
A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)

A hayye sama ado kasa kudi yan’matan duniya
A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)

Ey a hayye sama ado kasa kudi yan’matan duniya
A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)

A hayye sama ado kasa kudi yan’matan duniya
A hayye sama ruwa qasa ruwa samarin duniya (wazobiya)

Yan’matan duniya
Samarin duniya (wazobiya) x 5

Dinya
Samarin duniya (wazobiya) x 3

Sai da Dan Koya

Sai da Dan Koya
By Ashiru Nagoma

Uhmmm
Sai da dan koya akan yi gwani in ji Dan Auta
In har kana koya wata ran za ka zam gwani babba

[Chorus]
Uhmmm
Sai da dan koyo akan yi gwani in ji Dan Auta
In har kana koya wata ran za ka zam gwani babba

Uhmmm
Sai da dan koya akan yo gwani in ji Dan Auta
In har kana koya wata ran za ka zam gwani babba

Ina masoyana ga saqo na gaisuwa kyauta (uhmm Dan Auta)

Wannan masoyinku ne Nagoma Ashiru Dan Auta (uhmm Nagoma)

Wayanda ba sa so na ina so su zo mu sasanta (uhmm Dan Auta)

Da sannu sannu idan ka nay wata ran zaka zam babba

Chorus

Uhmmm
Idan ka ji ance wannan shi ya iya sosai (uhmm Dan Auta)

A can a baya sai da ya koya ya yi zama sosai (uhmm Nagoma)

Kafin ya samu abun da yake so ya ci wuya sosai (uhmm Dan Auta)

Yanzu ku dan lura ku fahimta shine gwani babba

Chorus

Ina mawakan Kaduna na zo ku zo ku shafan kai (uhmm Dan Auta)
Ina mawakan Kano ta Dabo ku zo ku shafan kai (uhmm Nagoma)
Ina mawakan Katsinawan Dikko ku zo ku shafan kai (uhmm Dan Auta)

Mawakan Zamfara ke bin na Sokoto ku zo ga Dan Auta

Chorus

Uhmmm
Sai da dan koya akan yi gwani in ji Dan Auta
In har kana koya wata ran za ka zam gwani babba

Chorus

Uhmmm
Sai da dan koya akan yi gwani in ji dan auta
In har kana koya wata ran zaka zam gwani babba

Chorus

Uhmmm
Ina matasa ina kiranku ku daina sa’insa (uhmm Dan Auta)

Baiwa ta Allahu ce ku gane mu daina yin gasa (uhmm Nagoma)

In Rabbi ya yarda lamuranka ba wanda zai amsa (uhmm Dan Auta)

Wannan misali ne a kaina baiwa ta Dan Auta

Chorus

Nigeria ha kasa ce ta gado mu daina tababa (uhmm Dan Auta)

Yawan fada shi ne ke kawo ana zaman gaba (uhmm Nagoma)

Sannan ya kan kawo tabarbarewa na arziki babba (uhmm Dan Auta)

Mu na kiran al’umma mu gane ku bar zaman gaba

Chorus

Zama na qarshe da magaifiyata tai min addu’a sosai (Allah ya amsa)
Zama na qarshe da Abba gare ni yay mani addua sosai (Allah ya karba)
Nima a yanzu garesu sai dai na yi addu’a sosai (Allah ya amsa)
Domin nay ladabi da biyayya Allah ka dafa min

Chorus