Gulma Wuya

Gulma Wuya
By Dan Maraya Jos

Sannan kun san boka dabam
Yar koren boka ma dabam
Gulma-wuya mai sha’anin tsiya
Mai son raba sunnar Rabbana
Kwatsam! O sai gat a cikin gida
Mai gidan nan na nan kin jiya
Shin a a ko ko ya fita
Sai ka ji dai matar gida
Ta cane O ai malam ya fita
Ta sami kujera nan da nan
Ga labara dan kadan
Na jiwo ne can ko a anguwa
Malam zai maki kishiya
Sai ka ji dai matar gida
Ta buga kirji nan da nan
Yanzu malam zai min kishiya?
Sai ka ji yar kore kuma
Ta ce mata lalle ai kuwa
Malam zai miki kishiya
Wannan ba shakka kuwa
Dagan an sannan in na tuna
Sai ka ji dai matar gida
Ta ce o yaya za na yi
Yar kore ta fada mata
Akwai wani bako nan a can
Can layin su magajiya
Ki tambayi mai gida
Za ki je kuma barker haihuwa
Mu hade layin su Magajiya
Mai gida in ya zo nan gidan
Sai ka ji dai matar gida
Ta chane
Malam zan tafi anguwa
Zan je barker haihuwa
Sai ta dauki gyalenta ta lulluba
Su hade layin su Magajiya
Rankai rankai in ka jiya
To da ma tun kan su zo
Yar kooren boka dada
Ta je ta wajen boka kuma
Ta gaya masa kome ya sani
Ga can sun ishe boka kuwa
Assalamu alaikum
Ai da ma na san za ku zo
kasan nan ta nuna mini
Kasa ba ta karya kuwa
Abin da dai kasa ta gaya mini
Wai malam zai miki kishiya
Kina kuma neman Haihuwa
Wannan ko lallai haka yake
Ba shakka kuwa
To sai ka ji mata ta chane
Malamin nan lallai ina gani
Abin day a daman wajibi
To shi ne ya gaya mini
Sai ka ji malam ya chane
Sai ka ji da matar gida
Ta ce
Malam yaya za a yi
Akwai ko yadda za a yi
Lalle zan miki magani
Ki ba ni farin rago biyar
Turmin alawayyo guda biyar
Ki ba ni kudin ki sule dari
Ki bani karauni guda biyar
Yanzun zan miki magani
Sai ka ji dai matar gida
Ta chane masa
Wannan abu mai sauki kuwa
Bari zan je chan ko cikin gida
Ta koma can gida
JAwo kwalla sayar
Jawo bokiti ma sayar
Ta tarar ta mika kudin
An kai wa boka nan da nan
Boka ya tattare
Boka ya handame
Je ki Allah zai mana magani