Da Ganinki

Da Ganinki
Umar M Shareef

Ehh da ganinki sai nakamo
Gashi kin zamo jinin jikina
Lokaci guda nakamo ooooh oohhh ooh

Aha aha aahaa
Aha aha aahaa aaaaah

Eh kallo daya bisa kallo ida nayi miki
Zuciyata sai ta kamo yan mata
Shi bari da ba’a yi mar ga damina
Zo a gareki sannu sannu yar gata
Banzo da matstsala ba
Ban zarce ka’ida ba
Ki yi min iso na zo gunki tunda kin ga ba koshi ba abin guduba

Na amsa sallamarka taho ga mazaun
Ka farta zantu kanka
Al’umma rahama ce
Har da kai ciki haka yaka ban gudunka
Manufarka bansaniba
Ban gani cikin ido ba
Ni dai fata nake komai zan ji ya zamo al khairi ina maraba

Baki gane me nake nufi ba
Soyayya ce nazo da ita
Da ita da ita
Kallo daya da nayi miki na na san macen da nakeso nayi gamo da ita
Da ita da ita
In jira bazan iyaba
Zantukan da na yi ki duba
Soyayya ce nake so ki bani inna samo zargi ba zan saki ba

Aha aha aahaa
Aha aha aahaa aaaaah

Uhm na yarda na yarda na amince
Yarda da kai taho mu kulla
Tsarinka lafazinka su suka sace
Zuciya tayi jimilla
Ba zan gujeka yiba
Nai caraf sonka na karba
Ni da kai kawai mu tsaro soyayya sabuwa
Karshenta na da riba

Nagode, nagode nayi murna mai zan biya tukuici
Ba komai ba komai tunda ka yaba
So ne shine tukuici
Lallai na zo da sa’a sai hamdala
Kin yi min karamci
Soyayya ce ta sanya
Komai ba zan gaza ba